Hausa Channel
04/04/2026
Shekaru Sha Shida 16 Kenan da Rasuwar Alhaji Abubakar Rimi
A irin wannan rana ta 4 ga watan Afrilu shekarar 2010 Allah yayi wa tsohon gwamnan Jihar Kano, marigayi Alhaji Abubakar Rimi, rasuwar.
A lokacin da yake raye,Rimi ya yi fice a siyasar Najeriya, inda aka san shi da kishin talakawa da kuma ƙoƙarin kawo sauyi, abin da ya sa ake masa laƙabi da “Limamin canji”.
Ina an ce Abubakar Rimi me kuke tunawa?
27/02/2026
JIYA BA YAU BA Gidan Sarkin zazzau kenan a Shekarar 1960. Allah ya jiƙan magabatan mu
27/02/2026
Masallacin Jumma'a Nomans Land, Sabon Gari a Kano, Tabbas Indai a Kano Kake kasan wannan Masallacin. Masallaci ne da Alhaji G. A. Bello (Criss Cross) ya gina da zunzurutun kuɗi ₦300,000, kuma aka buɗe shi ranar 26/02/1982. Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero ne ya buɗe, yayin da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji
Muhammadu Abubakar Rimi, ya zama, babban bako a wajen bikin.
Allah ya jiƙan Magabatanmu
26/02/2026
An ɗauki wannan hoto jim kaɗan bayan karɓar 'yancin Kan Nigeria, 1 ga watan Oktoba na shekarar 1960.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the public figure
Telephone
Website
Address
Kofar Nassarawa
Kano