Kokiya
09/06/2026
SUBHANALLAHI: Daya daga cikin dattawan da aka yi garkuwa da su a Jihar Kebbi, Malam Yahaya Billi, ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane.
Ƙungiyar Izalah JIBWIS reshen Ƙaramar Hukumar Koko-Besse ta sanar da rasuwarsa, tare da bayyana cewa za a gudanar da Sallar Jana'izar Ga'ib da ƙarfe 4:30 na yammacin yau a ƙofar gidan Sarkin Koko.
07/06/2026
Wike ya kare matakan sauye sauyen tattalin arziki da Tinubu ke aiwatar wa
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa jagoranci da jajircewar Shugaba Bola Ahmed Tinubu na taimakawa wajen rage gibin ababen more rayuwa a Najeriya.
Wike ya bayyana hakan ne yayin gabatar da lacca a bikin yaye dalibai karo na 36 na jami'ar Port Harcourt, inda ya ce ci gaban ababen more rayuwa na daga cikin muhimman alamomin ingantaccen shugabanci.
Ya yabawa gwamnatin Tinubu kan aiwatar da manyan ayyuka k**ar titunan Lagos-Calabar, Sokoto-Badagry, Abuja-Kaduna-Zaria-Kano, East-West Road da hanyoyin shiga gadar Niger ta biyu, tare da gyaran layin dogo na Port Harcourt zuwa Maiduguri.
Ministan ya kuma ce shirye-shiryen samar da wutar lantarki, gidaje, sadarwa, tsaro da ilimi, ciki har da asusun lamunin dalibai na NELFUND, na kara samar da damammaki ga ‘yan Najeriya.
Wike ya kare cire tallafin man fetur, yana mai cewa matakin ya samar wa gwamnatoci karin kudaden da za su zuba a ayyukan ci gaba da ababen more rayuwa, yana mai jaddada cewa shugabanci mai kawo sauyi na bukatar daukar matakai masu wahala domin samun dorewar ci gaba a nan gaba.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Website
Address
Kano