Hausa Novels Only
08/09/2025
04/05/2024
BASADAUKIYA
Littafi Na Daya (1)
Part B.
Na Abdulaziz Sani M Gini
AA Misau Ke Magana
(Barkanmu da wannan lokaci Yan uwa)
Ya tafi taga-taga zai kife da fuskarsa, sai da ya dage iya
Karfinsa sannan ya iya tsaida kansa. A lokacin ne
sauran dakarun da ke kewaye da ita s**a zare mak**ai
s**a yunkura za su afka mata. Amma sai s**a ji
Husaru ya daka musu tsawa yana mai basu umarnin su
dakata. Gaba dayansu sai s**a tsaitsaya. Husaru ya
mike tsaye ya juyo ya dubi matar Mujahid cikin
tsananin mamaki, domin wannan ne karo na farko da
wani mahaluki ya taba samun damar murde hannunsa
bare ma har a kusan kaishi kasa. Babban abin da ya
jefa Husaru cikin takaici shi ne 'ya mace ce ta
wulakantashi haka a gaban dakarunsa wadanda s**a
tabbatar da jarumtakarsa.
Husaru ya zare takobinsa ya durfafi matar
Mujahid gadan-gadan. Koda ganin haka sai itama ta
zare wata takobi da ke rataye a kafadarta ta nufeshi ba
da shakkar komai ba. Sai da ya rage saura baifi taku
uku ba su hadu sai kawai aka ga Mujahid ya dako
tsalle ya dira a tsakiyarsu. Nan fa aka fara kallon-kallo
tsakanin Mujahid da Husaru. Ita kuwa matar Mujahid
sai ta koma gefe daya ta zauna tana lura da motsin
sauran dakarun.
Mujahid da Husaru s**a fara zagaya juna
kowannensu na lura da motsin dan uwansa, ko kifta
idanu ba sa yi. Kai da gani ka san cewa kowannensu
ya kware a iya yaki, kuma sun san mak**a da lago.
Bayan sun zagaya juna k**ar sau uku sai s**a
kacame da azababben yaki, suna masu kaiwa juna sara
da s**a cikin tsananin zafin nama, juriya da bajinta
tamkar jikinsu ba na jini da tsoka bane
Sai da s**a shafe lokaci mai dan tsawo a haka
dayansu bai sami nasarar komai ba. Koda ganin haka
sai Mujahid ya sauya salon fada ya fara tsalle-tsalle da
yin alkafira a sama tamkar ba ya jin nauyin jikinsa, ko
kuma yana da fuka-fukai irin na tsuntsaye
Nan da nan Mujahid ya fara rikirkita Husaru ya
zamana cewa yana shawagi a samansa tamkar baiyanar
walkiya da bacewarta. Nan fa ya zamana cewa Husaru
baya iya mai da martani sai kokarin kare kai. Babban
abin da ya tayarwa da Mujahid hankali shi ne duk
sa'adda ya sari jikin Husaru sai yaji k**ar dutse ya
sara. Shi kuwa Husaru ya kasa taba jikin Mujahid.
Lokacin da wannan gumurzu nasu ya kara
tsamari, sai Husaru ya fara amfani da karfin sihiri yana
watsawa Mujahid wuta, kibiyoyi da tsitakoki, amma
sai ya ga wadanann mugayen abubuwan sun kasa tasiri
a jikin Mujahid. Ba komai ne ya haddasa hakan ba
face addu'ar da Mujahid ya fara yi. Al'amarin da ya
dugunzuma hankalin Husaru ke nan, ya tabbatar da
cewa yau fa watan jin kunyarsa ya k**a, don haka sai
ya kara zage dantse iya karfinsa yana kokarin ya kai
Mujahid kasa da Karfin tsiya. Shi kuwa Mujahid ya ki
Zuwa kasan.
Bisa mamaki Sai Mujahid ya ga ya sami nasarar
yankar jikin Husaru a cinya har jini ya zuba. Cikin
razana Husaru ya ja da baya yana mai dafe raunin ya
Kurawa Mujahid idanu ciki mamaki. Ashe ba wani abu
bane ya janyo samun Wannan nasara ba face addu'ar da
Muiahid ya fara karantawa a ransa, wacce ta tarwatsa
sirrin tsafin Husaru.
Ya yin da sauran Dakarun s**a ga Mujahid ya
sami Wannan nasara akan shugabansu sai s**a taso
gaba dayansu s**a afka masa.
Wohoho! Nan fa wuri ya sake yamutscwa. Koda
Matar Mujahid ta ga an yiwa mijinta rubdugu sai ta
yunkura da nufin ta kawo masa dauki, amma sai ya yi
ma ta nuni da kada ta zo, baya bukatar agaji, don haka
sai ta koma tayi zamanta. Shi kuwa ya ci gaba da
fafatawa da su ya zamana cewa ya zame musu
alakakai. Abin da ya daurewa dakarun kai shi ne baya
son ya cutar da su, amma sai yai ta bugunsu yana
zubar da su kasa. Nan da nan Mujahid ya fara yin laga-
laga da su, sai gasu a zube kasa magashiyan sun kasa
tashi. Koda ganin haka sai Husaru ya yi kururuwa
cikin matukar fishi yai įifa da takobin hannunsa ya
rugo izuwa kan Mujahid da mugun nufi. Koda matar
Mujahid ta hango abin da ke shirin afkuwa ta tabbatar
da cewa idan har Husaru ya riski mijinta zai iya yi
masa mugun lahani, sai kawai ta daka tsalle a sama
daga inda take zaune tana mai karanta wata addu'a. Sai
ta tafi shuuu! K**ar an cillata daga cikin baka. Kawai
sai agni aka yi ta doki kirjin Husaru da kafafunta biyu.
Take Husaru yai samna tamkar an cillata daga cikin
baka. Kawai sai gani aka yi ta doki kirjin Husaru da
kafafunta biyu. Take Husaru yai sama tamkar an
janyeshi da kugiya yaje ya manne a jikin ginin rijiyar
nan ya sulale kasa sumamme, jini na zuba ta cikin
hanci da baki.
Koda ganin abin da ya faru sai ragowar dakarun
nan dake zube a kasa a galabaice s**a mike zumbur
s**a tsere. Ba komai ne ya haddasa hakan ba face basu
taba ganin mutumin da ya taba kai Husarukasa ba, sai
yau. Babban abin mamakin ma shi ne, ya mace ce ta
kaishi kasa.
Bayan gaba daya Dakarun sun gudu sai Mujahid
ya dubi matarsa yai murmushi ya ce "Yake Sakinat
mu yi sauri mu kada Rakumanmu izuwa cikin kasuwa
mu nemi masauki tun kafin a sake turo wadansu
dakarun da za su yiwa dukiyarmu barna".
Koda jin wannan batu sai Sakinat ta dubi mijinta
cikin matukar damuiwa ta ce, "Ai ni abin da nake tsoro
ma shi ne, za a iya binmnu har cikin kasuwar a kashe
mana Rakuma kuma a kwashe mana haja."
AA Misau ke magana
Koda jin haka sai Mujahid yai murmushi ya ce,
"Kada ki damu ya matata, ai addu'a makamin
muminice, mu ci gaba da yin addu'a da yardar Allan
babu abin da zai samemu ko dukiyarmu".'
Koda gama fadin haka sai Mujahid ya kada
Rakuman, Sakinat ta taimaka masa s**a nufi hanyar
Masu iya magana sun ce idan ka je gari ka ga
jama 'ar garin na da jela, kaima sai ka nemi tsumma ka
daura, domin ka zauna lafiya ba don kana so ba.
Lokacin da Mujahid da Sakinat s**a iso kasuwa,
sai ya lura cewa mutanen birnin masu kwadayi ne
matuka da son abin duniya. Sabo da Mujahid yana son
Rakumansa da dukiyarsa su tsira sai ya kira Sarkin
kasuwa gefe ya yi masa alheri na dinare dari ya ce da
shi, yana da rakuma guda dari uku da sittin da biyu,
yana neman wurin da zai adana wadannan rakuma da
hajojinsu, inda babu wanda zai iya yi masa 6arna".
Koda jin wannan batu sai Sarkin kasuwa ya ce,
"Shi yana da wuri mai matukar sirri, amma nawa zai
biyashi ya yi masa gadin dukiyar tasa?". Mujahid ya
ce, "Zan baka dinare dari biyar". Sarkin kasuwa ya ce,
"A'a ba zan karbi hakan ba, domin wannan aiki da zan
yi maka mai hadarin gaske ne. Na sani cewa baka kai
dukiyarka gaban Sarauniya ba, domin inda ka kaita da
tuni ta rabaka da rabinta, al'adarta ke nan. Idan
Sarauniya ta fuskanci cewa ni ne na 6oye maka
dukiyarka za ta iya sawa a kaini kurkuku kuma a
rabani da duk abin da na mallaka. Idan har kana son na
boye maka wannan dukiya sai dai ka biyani dinare
dubu uku. Kuma ka sani cewa kai kanka da wannan
matar taka kuna cikin hadari, dole ne kuma ku buya".
Koda jin haka sai Mujahid ya cika da
mamaki
,"To wai shin ita wannan Sarauniya taku wace irin
dabi'ace da ita ne? Bayan ta kwacewa mutum dukiya
kuma shima sai ta zalunceshi?".
Sarkin kasuwa yai ajiyar zuciya sannan ya ce,
"Ya kai wannan bako, kayi sani cewa duk da ban ga
fuskarka ba a yanzu na fahimci cewa kai kyakkyawa
ne, haka ma matarka, domin da idanunku kawai na
lura da hakan. Kuyi sani cewa Sarauniyarmu batau
taba yin aure ba, kuma bata taba haihuwa ba, amma
tana da wata muguwar dabi'a wadda duk sa'adda ta ga
saurayi kyakkyawa sai tayi lalata da shi, sai ta sa
akaishi wani kurkuku mai suna Sijinil Maut a tsareshi
đaurin rai da rai. Tabbas idan Sarauniya tayi arba da
kai sai hakan ta faru gareka.
Ita kuwa wannan kyakkyawar mata taka ta zama
kuyangarta ke nan mai yi ma ta hidima."
Koda Mujahid da Sakinat s**a ji wannan batu,
sai hankalinsu ya dugunzuma. Sabo da haka sai s**a
amince da bukatar sarkin kasuwa s**a bashi dinare
dubu uku. Nan take sarkin kasuwa ya sa aka kada
Rakuman su Mujahid izuwa cikin wani katon kango.
Bayan Rakuman sun gama shiga sai aka rufe kofar
kangon ya zamana cewa daga sarkin kasuwa sai su
Mujahid ne kadai a cikin kangon, wato su uku rak.
Kawai sai s**a ga sarkin kasuwa ya shiga daga wasıu
dammai na ciyawa. Gama yin haka ke da wuya sai ga
murfin wata tsohuwar rijiya mai fadi sosai. Sarkin
kasuwa ya bude wannan murfin rijiya sai ga hanya
azururu izuwa gidan kasa. Sarkin kasuwa ya k**a
akalar Rakumin da ke kan gaba ya jashi izuwa cikin
wannan gida na karkashin kasa yana mai cewa da su
Mujahid, "Ku koro ragowar Rakuman su biyo
bayanmu". Ba tare da wata gardama ba s**a bi wannan
umarni. Kawai sai tsintar kansu s**a yi a cikin wani
wangamemen gida mai yalwar fadi da dakouna
barkatai, har da rijiya. Kuma ga wasu hadiman mata su
bakwai suna ta dan aikace-aikace. Al'amarin da ya
đaurewa Mujahid da matarsa Sakinat kai ke nan, s**a
cika da mamaki, domin basu taba tsammanin wajen zai
kasance haka ba.
Koda Hadiman matan nan su balkwai s**a hango
sarkin kasuwa janye da Rakuma da kuma baki sai s**a
tarbeshi cikin murna. Nan take s**a taimaka masu
wajen kora rakuman izuwa cikin babban filin s**a
zazzaunar da su kasa, sannan s**a shiga sauke hajojin
da ke kansu. Babu abin da ya kara baiwa su Mujahid
mamaki face yadda matan bakwai s**a zage damtse
suke aiki tamkar ba mata ba. Sai da aka kallama sauke
kayan gaba daya, sannan Sarkin kasuwa ya yiwa su
Mujahid jagora izuwa wani đaki mai kyau wanda aka
shimfida kilishi mai taushi a cikinsa. Da shigarsu cikin
dakin sai s**a zauna su ukun sannan daya daga cikin
hadiman matan nan ta kawowa su Mujahid abinci mai
kyau gami da ruwan sha ta ajiye a gabansu ta fita.
Fitarta ke da wuya sai Sarkin kasuwa ya dubi
Mujahid ya ce, "Ya kai wannan attajirin bako ku saki
jikinku kai da matarka, kuyi zamanku anan cikin
kwanciyar hankali, kada ku kuskura ku fita waje har
Izuwa gobe da safe, sa'adda kasuwa za ta fara ci. A
goben ma ku 6atar da k**anninku sosai. Ka
shawartawa matarka tayi zamanta anan in ya so kai ka
fita ka siyar da hajarku. Ina mai dada shawartarka da
hajar ta ka ma a rinka fita da ita da kadan-kadan har ta
kare, domin tabbas Sarauniya za ta turo nemanku da
dukiyarku. Yanzu dai ku abni labari mene ne ya faru
tsakaninku da Dakarun Sarauniya?".
Koda jin wannan tambaya sai Mujahid da Sakinat
s**a dubi juna, sannan Mujahid ya ce, "Yanzu wane
tabbaci za ka bani cewa ba za ka ci amanarmu ba ka
tona mana asiri?".
Sarkin kasuwa ya yi murmushi ya ce, "Babban
tabbaci shi ne abin da na yi muku yanzu. In da ina son
na tona muku asiri da ban baku mafaka kun 6uya ba ku
da dukiyarku. Abin da na ke so ku fahimta shi ne, gaba
daya mutanen wannan birni namu bama kaunar
zaluncinta da rashin tausayinta ga kowa. Ni kaina din
nan duk bayan kwana talatin sai na biya haraji mai
soka Na taimake ka ne ba don komai ba sai domin
dukiyarka".
Sa'adda Sarkin kasuwa ya zo nan a zancensa sai
Mujahid ya yi murmushi da godiya a gareshi, sannan
s**a yi sallama ya fita ya barsu su biyu rak a wannan
đaki.
Fitar Sarkin kasuwa ke da wuya sai Sakinat ta
dubi mijinta Mujahid cikin damauwa ta ce, "Ya kai
mijina ni fa hankalina atashe yake bisa jin dabi'ar
wannan Sarauniya akan kyawawan samari. Ina tsoron
kada ta sami nasara akanka".
Koda jin haka sai Mujahid ya cire rawanin kansa
ya taso daga inda yake zaune ya dawo inda take ya cire
nata rawainin s**a dubi kyawan fuskokinsu, sannan ya
yi murmushi a gareta ya ce, "Kwantar da hankalinki ya
abar kaunata da izinin Allah babu abin da zai faru
gareni. Kin sani cewa addu'a makamin mumini ce, don
haka Allah zai karemu daga dukkan sharrin wannan
mata."
Ya yin da Sakinat taji haka sai farin ciki ya
shigeta ta rungume Mujahid tana mai sumbatar
goshinsa ta ce, "Hakika ka gama magana ya mijina,
tabbas addu'a ce maganin fasikan wannan zamani.
Wannan shi ne abin da ya faru tsakanin Mujahid
da matarsa Sakina bayan Sarkin kasuwa ya boyesu tare
da dukiyarsu a cikin gidan kasuwa wanda ya kasance
boyayye.
A CAN FADAR Sarauniya Dulaiba kuwa,
Lbayan k**ar sa'a daya da fitar Sarkin yaki
Hasaru sai ga daya daga cikin dakarunsa ya shigo
cikin fadar jina-jina yana tafiya yana layi. Al'amarin da
ya razana gaba dayan jama'ar da ke cikin fadar ke nan,
s**a mimmike tsaye. Ita kanta Sarauniya Dulaiba bata
san sa'adda ta mike tsaye ba.
Badakaren ya isa daf da karagar Sarauniya
Dulaiba, sai ya yanke jiki ya fadi yana numfashi da
kyar, sannan ya bude baki a cikin matukar karfin halí
ya ce, "Ya shugabata kiyi sani cewa yau wasu
hatsabiban baki ne s**a shigo wadanda s**a kasance
sadaukai na gaban kwatance su biyu mijii da mata. A
halin yanzu sun sumar da Sarkin yaki Hasaru da
dukkanin dakaru dubun da yaje da su. Bayan mun
farfado ne. duk muka tsere muka nausa cikin gari a
firgice ni kadai ne ban rude ba nayi tunanin na dawo
nan na bada labari".
Sa'adda Badakaren ya zo nan a jawabinsa sai
zuciyar Sarauniya Dulaiba ta k**a tafarfasa tamkar za
ta konc, sabo da bakin ciki. Cikin tsananin fushí ta
dubi boka Gaihar ibni Sabbur ta ce, "Ya kai abin
dogarona, maza kayi bincike ga gano mini inda
wadannan baki suke a yanzu, kuma ko ta yaya ina son
muje yanzu ni da ku mu kamosu".
Topah Nima A A Misau a nan zandakata saikuma wani Lokaci
Karku manta zaku iya binmu a WhatsApp group dinmu wanda zaku dinga samun LITATTAFAN yaki dana soyayyah harda Na nishadi 👇👇👇👇
https://chat.whatsapp.com/E0GMznXcaxwC0avNVdF30Q
Sannan a Facebook ma haka
Zaka iya samunmu a wadannan shafuka
Saikunzo
AA Misau Ke Magana
28/04/2024
GUGUWAR ANNOBA
Littafi Na Daya (1)
Part D.
Na Abdulaziz Sani M/Gini
AA Misau Ke Magana
(Karku Manta Zaku samemu a WhatsApp grp namu ta link da ke kasa
Bayan Nan ina Mana Barka da wannan lokaci)
Marubucin yaci GABA da cewa...
Abin tambaya anan shi ne, "Ta ya ya wannan
sohon mutum ya iya daukar Wannan sungumi mai
naUyi a bayansa alhalin sungumi ne mai gima da
Idan mutum ya lura da kirar jikin tsohon
wacce ta kasance irin ta samudawa zai iya baiwa
kansa amsa cewa ai karfi yana ga mai alamar Kiba.
Kai tsaye Sarki ya nufi inda kujerar mulkinsa
take tare da bakinsa mutum biyu. Koda ganin haka
sai 'yan majalisa s**a mike tsaye don girmamawa.
Da isarsu daf da karagar mulki sai Sarki Yarduza
ya k**awa tsohon wannan katon sungumi da ke
bayansa ya ajiye a kas, sannan ya tsohon ya yi
masa umarni da ya hau kan karagarsa ta mulki ya
Zauna.
Gaba dayan jama'ar da ke cikin fadar sai s**a
bude baki s**a kurawa Sarki idanu cikin tsananin
mamaki, aka rasa wanda zai cc kala.
Sarki Yarduza ya dubi Sharlisa ya nuna ma ta
wata kujerar da ke daf da karagar mulki ya ce itama
ta zauna. Sharlisa taje ta zauna sannan Sarki
Yarduza ya tsaya a gabansu ya fuskanci fadawansa
da sauran jama'a ya ce,"Ya ku jama'ar Birnin
Kaluza ku yi sani cewa wadannan baki da nazo da
Su yanzu sun kasance masu matukar daraja a
idanuna, saboda haka daga yau ina son ayi biyayya
wannan tsoho da ke zaune akan karagata k**ar
yadda ake yi mini har izuwa tsawon kwana bakwai.
Duk irin abinda ake yi mini shi nake so dinga yi
masa. Kada a rage masa abu daya".
Koda gama fadin hakan sai Sarki Yarduza
koma gefe daya ya zauna a kasa dirshan kusa da
karagar mulki tamkar almajiri, sannan aka ci gaba
da tafiyar da harkokin mulki.
Al'amarin da ya matukar baiwa gaba dayan
mutanen da ke fadar mamaki ke nan kuma ya
dugunzuna hankalin 'yan majalisa.
Daga can sai shugaban Majalisa yazo ya
zauna daf da Sarki Yarduza yai masa rada a kunne
ya ce, "Ya shugabana wannan abu da kayi yanzu
bai taba faruwa ba a wannan masarauta tamu,
tabbas abin kunya ne kuma abin gori ne
zuri'arku"..
Koda jin wannan batu sai Sarki Yarduza ya
d**o kai ya dubeshi cikin tsananin fishi da fusata
ba tare da ya ce komai ba. Nan take jikin shugaban
majalisa ya k**a karkarwa, domin
ya san cewa
Cikin sanyin jiki shugaban majalisa ya mike
tsaye ya koma inda yake ya zauna.
Kuraisu ya k**a kallon karagar mulkin da
yake zaune a kanta tamkar dan kauye ya shigo
Birni, sannan ya rinka kallon fadawa da sauran
jama ar gari da kuma sauran kayan kawar da ke
fadar.
Daga can sai ya mike tsaye ya k**a yawo a
ikin fadar yana taba kayayyaki yana kyalkyala
ariva cikin tsananin farin ciki tamkar mahaukaci
sabon kamu.
Daga can sai ya koma kan karagar mulki ya
zauna. Kawai kuma sai aka ga ya fashe da kuka.
Koda ganin haka sai idanun Sharlisa da na Sarki
Yarduza s**a ciko da kwalla s**a k**a zubar da
hawaye, saboda tausayinsa, domin su kadai ne s**a
san dalilin dariyarsa da kukansa.
Sauran jama'a kuwa duk s**a cika da tsananin
mamaki bisa wannan bakon al'amari.
K**ar yadda Sarki Yarduza ya bayar da
umarni, haka al'amarin ya kasance, wato sai da
Kuraisu ya kwana bakwai kullum yana zama akan
karagar mulki yana shugabantar jama'ar Birnin
Kaluza, kuma yana kwana a gadon Sarki Yarduza,
yana sanya suturarsa da cin irin abincinsa.
Babu abinda ya kara daurewa mutane kai face
ganin yadda Kuraisu ke tafiyar da harkokin mulki
dai-dai k**ar yadda kowanne Sarki da ya shude ke
yi, tamkar dama can a gidan sarautar ya taso, ya
san komai ba a koya masa ba.
'Yan majalisa kuwa, s**a yi ta zunde da
munafunci a tsakaninsu suna ta
gano ko wane ne wannan bakon tsoho da Sarki
Yarduza ya zo da shi ya daukakeshi fiye da kansa
bincike akan s
Abinda kawai s**a iya ganowa shi ne, tsohon
ya kasance uba ga wannan kyakkyawar budurwa
wacce Sarki ya zo da ita.
A daren kwana na bakwai ne tsoho Kuraisu ya
kamu da tsananin zazzabi mai zafin gaske, jikinsa
ya k**a tsuma, yana kwance akan gado a cikin
turakar Sarki, 'yarsa Sharlisa na zaune daf da shi
cikin tsananin dimauta da tashin hankali, domin a
iya zamanta da mahaifin na ta bata taba ganin sa ba
Sharlisa ta kurawa Kuraisu idanu a lokacin da
hawaye ke zuba daga cikin idanunsu su biyun, ta
k**a kafadunsa ta rike tana mai cewa, "Ya kai
Abbana kayi sani cewa a tsawon zamana da kai ban
taba ganin ranar da ka yi koda ciwon kai ba, amma
yau gashi zazzabi mai zafi ya rufeka, kuma
Likitoci sama da guda hudu sun shigo sun dubata
da kuma dalilin yin hakan, amma s**a kasa.
a cikin irin wannan hali ba.
Sun baka magani ka sha amma har yanzu baka sami
latiya ba, mene ne ma'anar wannan rashin lafiya?"
hannunsa da kyar ya k**a hannun Sharlisa ya ce,
Sa adda Kuraisu yaji wannan tambaya sai ya daga
ya ke 'yata ki gafarceni, domin kuwa na 6oye
miki wani babban al'amari a rayuwata.
Tabbas numfashina a duniya yau zai yanke, a
vau ne mai rabawa za ta rabamu, domin wa'adina
ya cika.
Tun daga ranar da dan uwana Yarduza ya hau
kan karagar mulkin kasar nan, wato mahaifin Sarki
Yarduza na yanzu, wanda ya kawo mu fadar nan,
na bazama yawo wajen bokayen duniya ina neman
sihirin da zan iya hallakashi na yi masa juyin mulki
A ranar da aka haifcki ne na sadu da wani
hatsabibin boka ya ce da ni har abada ba zan iyama
komawa cikin Binin Kaluza ba sai bayan mutuwar
dan uwana a zamanin mnulkin dansa, kuma a
nan din Tna sai dai na dandani mulki na tsawon
kwana bakwai kacal, kuma a daren kwana na
Bokan ya ce da ni idan har na amince zai iya
yi mini sihirin da wannan bukata tawa za ta biya.
da karfin tsiya a darc daya, amma ban samu ba har
izuwa lokaicn da mahaifiyarki ta haifeki.
bakwan zan mutu.
Koda na ji wannan batu sai hankalina ya
dugunzuma na fashe da kukan bakin ciki saboda na
auna na ga cewa wannan dama fa sa'adda za ta zo
mini na tsufa ainun, kuma mene ne amfanin naji
dadin mulkin gidanmu na kwana bakwai kacal?
Sai da na dade ina tunani da zullumi gami da
matsanaicin bakin ciki, daga bisani sai zuciyata ta
ce da ni, "Ai idan ma ban yi amfani da wanna
dama ba dole dai mutuwa zan yI na bar duniya ba
tare da na cik aburina ba,"
Nan take na amince da sharadin wannan boka
ya yi mini wannan sihiri. labbas tsafi gaskiyar mai
shi ne, domin gashi yanzu wannan tsafi ya yi
tasirinsa.
Ya ke 'yata, kiyi sani cewa lallai ina ji a jikina
cewa a ko yaushe ruhina zai iya fita daga cikin
gangar jikina. Ma za ki ruga ki je ki nemo Sarki
Yarduza domin na bar masa wasiyya da amanarki".
Koda jin wannan umarni sai Sharlisa ta fashe
da matsanaicin kuka, ta kwanta akan kirjin Kuraisu
Kwatsam! Sai s**a ji an bude kofar turakar,
Sharlisa ta juyo da sauri, sai ta ga ashe Sarkı
Yarduza ne ya shigo.
Koda ya hango Sharlisa kwance akan kirjin
ta kasa tashi ta tafi kiran Sarki Yarduza.
Kuraisu tana ta faman sharba kuka sai hankalinsa
ya dugunzuma ainun ya rugo garesu ya zauna a
geten gadon ya k**a hannun Kuraisu ya rungume
kirjinsa, shima idanunsa s**a ciko da kwalla.
Kuraisu ya dubi Yarduza cikin murmushin
karfin hali ya ce, "Ya kai dana, kayi sani cewa
vanzu zan tafi izuwa inda mahaifinka ya tafi, kuma
ina matukar farin ciki da ya kasance zan tafi a
lokacin da na sami damar ganawa da kai.
Wasiyata a gareka ita ce, ga 'yata nan na baka
ita halak, malak! Kuma ka riketa amma ka ci gaba
da jiyar da ita irin dadin da ka jiyar da ni tsawon
kwanakin nan bakwai har izuwa ranar da mutuwa
za ta rabaku.
Tabbas idan kayi haka za ka yi nisan kwana,
kuma za ka sami magaji. Idan kuwa ka bijirewa
wannan umarni nawa mulkin kasar nan zai bar
hannun zuri'arnu har abada, kuma ba za ka ta6a
samun magaji ba wanda zai cika maka naka burin
k**ar yadda ka cika na mahaifinka".
Koda Kuraisu yazo nan a zancensa sai jikinsa
ya k**a karkarwa mai karfi, idanunsa s**a kafe.
Sharlisa ta ciccibeshi cikin matukar firgici ta
rungumeshi a kirjinta tana mai fashewa da kuka.
Daga can sai taji jikin nasa gaba daya ya
AA Misau Ke Magana
sandare ko motsi baya yi, kawai sai ta dada
kankameshi ta fashe da wani sabon matsanaicin
kukan.
Da kyar Sarki Yarduza ya bambareta daga
jikin gawar mahaifin na ta.
Sharlisa ta rungume Yarduza ta ci gaba da
kuka, shima sai zuciyarsa ta karaya ya k**a kukan
mazaje yana zubar da hawaye kawai.
A dai-dai lokacin ne Dakaru s**a shigo cikin
turakar s**a dauki gawar Kuraisu s**a fita da ita
domin a fara shirye-shiryen bikin binneta.
Bayan kwana uku da binne gawar tsoho
Kuraisu a inda aka saba binne duk Sarakunan da
s**a yi mulki a gidan sarautar, sai Sarki Kuraisu ya
ki ci gaba da zaman fada bare ya ci gaba da zartar
da sauran harkokin mulki.
Al'amarin da ya dugunzuma hankalin 'yan
majalisar ke nan s**a yi gangami s**a zo s**a
sameshi har cikin turakarsa.
A wannan lokaci yana tare da Sharlisa yana
rarrashinta da lallaminta domin ta ci abinci, saboda
tunda mahaifinta ya rasu sau daya ta ci abinci loma
uku kacal, har ta rame ta fita haiyacinta.
A sannan ne Yarduza ya shawo kan Sharlisa
ta ci abinci mai dan yawa har ta koshi ta sha ruwa.
Koda Sarki Yarduza ya ga 'yan majalisa Sun
shigo har cikin turakarsa sai ya mnike da sauri ya
dubi Sharlisa ya ce, "Ki jirani ina zuwa ya ke
masoyiyata,"
Cikin sauri ya tari 'yan majalisar ya fitar da su
waje kuma ya jasu s**a tafi izuwa can fada.
Da shigarsa cikin fadar sai yaje ya zauna a kasa
maimakon ya zauna a kan karagar mulki. Da ganin
haka sai suma 'yan majalisar duka s**a zazzauna a
kasa kusa da shi.
Tsawon 'yan dakiku kowa yai shiru bai ce
kala ba.
Daga can sai shugaban majalisar yai gyaran
murya ya ce, "Ya shugabana, kayi sani cewa
hankalinmu ya dugunzuma ainun saboda tunda
wannan bakon tsoho ya mutu baka fito fada ba.
Ai ya k**ata ace yanzu ka gama alhinin
rashinsa.
Abu na biyu shi ne, muna son ka gaya mana
matsayin wannan kyakkyawar budurwa da ka zo da
ita da kuma alakarta da wannan tsoho da ya mutu,
da kuma irin darajarsu a wajenka, domin mun ga ka
darajtasu fiye da kima".
Sa'adda shugaban majalisar yazo nan
zancensa sai Sarki Yarduza ya turbune fuskarsa
k**ar wanda aka aikowa da sakon mutuwa.
Al'amarin da ya frgita 'yan majalisar ke nan gaba
đayansu.
Sarki Yarduza ya dubi shugaban majalisa a
fusace ya daka masa tsawa ya ce,
"Sarki Sarki ne!
A ko yaushe duk abinda ya yi dai-dai ne. Babu
wata huja da za ta sa ku tuhumeni bisa abinda na
aikata, domin ba zan taba yin abinda na san zai
cutar da jama'ata ba ko kasata.
Duk irin jita-jitar da ake yi a garin nan da
gulma suna dawowa kunnena. Na san cewa kowa
so yake ya san sirrin da ke tsakanina da wadannan
baki da na kawo.
To ku sani cewa ko za ku san wannan sirri sai
dai bayan raina! Daga yau ni ba zan sake hawa kan
karagar mulki ba kuma ba zan bayar da umarnin
komai ba.
Wannan bakuwar budurwa da na zo da ita, ita
ce za ta ci gaba da zartar da komai. Wannan yana
nufin cewa ita SARAUNIYARKU!
Har gobc ni ne Sarkinku, kuma a gobe da safc
za a daura aurcna da ita. Na sallamcku kowa ya
k**a gabansa!"
Koda gama fadin hakan sai Sarki Yarduza ya
mike tsayc ya fice daga cikin fadar ya koma izuwa
i
cikin gidan sarautar ya bar yan majalisa a zaune
suna muzurai da kallon Juna cikin tsananin
mamakin jawabin da ya yi musu ya zamana cewa
on rasa wanda zai ce kala a cikinsu.
Kashe gari kuwa aka daura auren Sarki
Yarduza da Sharlisa, aka shiga shagalin biki.
Mawaka, Makada, Maroka s**a yi ta bidirinsu.
Sauran Sarakuna, Attajirai da masu fada aji na
kasashen makwabta s**a yi ta kawo ziyarar taya
murna da kawo kyauttuttuka, ya zamana cewa
Birnin Kaluza ya cika ya batse da mutane
Sai da aka kwana goma ana rakashewa sannan
Sarki ya sallami bakinsa aka watse.
Daga wannan rana Sharlisa ta zamo tamkar ita
ce Sarauniyar Birnin Kaluza, sai umarnin da ta
bayar shi ake bi.
Abinda ya kara daurewa jama'a kai shi ne, a
lokacin Sharlisa nc arzikin kasar ya bunkasa fiye
da ko yaushe, kuma alka sami zaman lafiya da
kwanciyar hankali irin wanda ba a taba samu ba a
tarihin mulkin masarautar da ya shude.
Kuma a sannan ne Dakaru s**a rinka samun
horon yaki na musamman irin wanda ba a taba
basu ba. Kuma Sharlisa ce take basu horon da
kanta.
A wannan lokaci ne labarin Sharlisa ya bazu a ko
ina nahiyar har ma aka fara tunanin tafi Sarki
Yarduza jarumtaka da iya yaki, saboda ganin wata
gagarumar bajinta da tayı bayan ta sami wata uku
cif akan karagar mulki.
Al'amarin ya faru ne wata rana, da rana tsaka
ana zaune a fada, Sharlisa na tafiyar da harkokin
A wannan lokaci mijinta Sarki
zaune a gefe daya yana kallonta kawai yana
murmushi cikin farin ciki.
Kwatsam! Sai ga wani babban
makiyayi da ake kira Zamaranu dan Bilsaru ya shigo fadar a
rude jina-jina. Da zuwa sai ya fadi gaban Sharlisa
yana haki k**ar ransa zai fita.
Da kyar ya budi baki ya ce, "Ya shugabata ki
yi sani cewa na fita bayan gari tare da dabbobin
jama'a, kimanin guda dubu saba'in tare da
Dakaruna su dari bakwai, domin mu gudanar da
kiwo k**ar yadda muka saba yi kullum a cikin
daii. sai kwatsam! MuKa ga Dakarun sumame
kimanin su dubu talatin sunyi mana
kawanya.
Ba tare da jiran komai ba s**a hau mu da sara
da s**a s**a karkashe dukkan yarana. Da kyar ni
kadai na sha na gudu izuwa nan cikin gari.
Abin takaici shi ne, ko alamar guduwa ma
basu yi ba, har na ji Shugabansu yana cewa naje na
gayawa wannan macen sarauniyar tamnu idan ta isa
tazo ta karba maku dabbobinku. Idan kuna ba za ta
a ba ta turo Dakarunta tunda yanzu mijinta ya
zama mace kamnar ita. tun
Kafin
makiyayi Zamaranu dan Bilsaru ya
gama rufe bakinsa tuni Sarki Yarduza ya zare
takobinsa cikin zafin nama ya fille masa kai. Take
kan ya fice fit daga jikin wuyansa yai sama ya fado
kasa kuma jini yai tsartuwa da fushi.
Gaba daya jikin Sarki Yarduza ya k**a
tsuma, kawai sai ya mike tsaye a fusace ya dubi
wani Badakare ya ce, "Aje a kawo masa
garkuwarsa da dokinsa zai fita shi kadai ya yaki
wadannan Dakarun sumame".
Koda jin wannan batu sai Sharlisa ta ce, "A
dakata". Kawai sai ta mike tsaye daga kan karagar
mulki ta tako ta zo gaban Yarduza ta tsaya, ta
dubeshi cikin murmushi ta ce da shi, "Haba ya kai
mijina, ai wannan karamin aiki ne, ka fi ga nan, sai
dai ni!
Ka sani cewa kai gwarzon sadaukai ne, baka
tarar iska sai dai GUGUWAR ANNOBA. Ka
kyaleni da wadannan marasa kunya ni ne zan yi maganinsu"
Gama fadin hakan ke da wuya sai ta karői
takobin da ke hannun Sarki Yarduza ta ruga da
gudu izuwa wajen fadar ta fita daga cikin harabar
gidan sarautar gaba daya ko doki ba ta nema ba.
Abinda ya fara baiwa jama'a mamaki shi ne,
ganin azababben gudun da take falfalawa tamkar
na doki, kuma babu alamar gajiya a tare da ita.
Kafin wani lokaci tuni ta fice gaba daya daga cikin
Birnin gaba daya.
Bayan Sharlisa ta fice daga cikin fadar
hankalin Sarki Yarduza ya dugunzuma ya fara
tunani a ransa ya ce, "Anya kuwa Sharlisa ba ta yi
ganganci ba? Ta ya ya za ta iya tarar wadancan
Dakarun sumame kimanin su dubu talatin ita
kadai?
To wai shin ma ta iya yaki ne sosai? Kuma
wacce irin juriya ce da ita? Shi dai bai taba ganin
yanayin yakinta ba, abinda ya taba gani kawai shi
ne, wannan jarumtaka da tayi ta kamo barewar da
va kasa k**awa sak**akon hawa kan tsauni mai
Santsin
Sa'adda Sarki Yarduza ya zo nan a zancen
Zucinsa sai hankalinsa ya dugunzuma ainun, nan
take ya mike zumbur! ya sake bada umarni aka
kawo nasa kayan yaki yai damara, sannan ya hau
doki ya zaburcshi da gudu izuwa wajen gidan sarautar
Nan take shugaban majalisa ya umarci
shugaban Dakaru ya ce maza su bi bayan Sarki
Warduza da matarsa su kai musu đauki.
Cikin gaggawa sama da Dakaru dubu arba'in
s**a yi hawa s**a bi bayan su.
AL'AMARIN JARUMA
SHARLISA
Akuwa, lokacin da ta ke falfala azababben
gudu ta fito daga cikin Birnin Kaluza, sai ta hango
dandazon Dakarun sumamen sun kafa sansani.
Saboda wulakanci ma har sun yanka
cikin dabbobin sun kunna wuta suna
wadansu daga
gasawa za su
Koda Dakarun sumamen s**a hango mutum
daya kacal ya fito daga cikin Birnin Kaluza a guje
ya durfafo sansaninsu sai s**a cika da tsananin
mamaki s**a mimmike tsaye s**a zuba idanu suna
jiran karasowar mutumin, domin su ga ko wane
mai tsaurin ido ne haka.
Koda Sharlisa ta iso daf da su sai tayi turjiya
ta tsaya tana haki ana kallon-kallo.
Ya yin da Dakarun sumame s**a ga ashe
mace ce sai gaba dayansu s**a bushe da darivar
mugunta. S**a yi ta kyalkyalawa k**ar ba za su
daina ba.
Kwatsam! Sai s**a ji Sharlisa ta daka musu
tsawa, tsawar da ta cika filin wajen gaba daya da
amsa kuwwa.
Gaba dayansu sai da s**a shiga taitayinsu
domin tsawa ce irin wacce manyan mazaje ke yi a
filin daga, ka ga mutane sun dimauce sun k**a
gudu suna neman maboya.
Sharlisa ta dubi Dakarun sumamen gaba
dayansu ta ce, "Ku kananan kwari, ku yi sani cewa
ni ce dan hakin da kuka raina mai tsokane muku
Tabbas yau kun yi babban kuskure, kuma
babban ganganci da kuka kawo hari nan Bimin
domin gwara ku je ku jefa kanku a cikin wutar da
ta shekara tana ci da ruruwa.
Na rantse da darajar wannan takobi ta sarautar
Bimin Kaluza da ke hannuna sai na zare muku
ruhin numfashinku gabe dayanku, dayanku ba zai
tsira da rayuwarsa ba."
Koda jin wannan
Dakarun sumamen s**a
batu sai gaba dayan
sake bushewa da dariyar mugunta lokaci guda Kuma s**a tsuke bakinsu
Topah Nima Kuma A A Misau Anan zan tsuke bakina nake cewa Sai wani lokaci Kuma
WhatsApp grp
Facebooks
AA Misau Ke Magana
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the organization
Telephone
Address
Hadejia
730102