Arewa Post

Arewa Post

Share

26/04/2026

Ɗan Gidan Marigayi Tsohon Shugaban Ƙasar Najeriya Yusuf Buhari Na Cigaba Da Yawan Neman Zaɓe.

Wane Fata Kuke Masa?

23/04/2026

Tsohon ɗan takarar Majalisar Jiha na Ƙaramar Hukumar Kabo a shekarar 2023, Hon. Rabi'u Sayyadi Kazode, ya fice daga jam’iyyar PDP.

Tun a ranar Litinin 20/4/2026 tsohon ɗan takarar ya bayyana ficewarsa daga tsohuwar jam'iyyar tasa, inda ya miƙawa shugaban jam'iyyar PDP a mazaɓarsa ta Masanawa takardar ficewar ta sa.

Yayin ficewar ta shi, ya godewa jagororin PDP dake mazaɓarsa, haka kuma ya jaddada cewa yanzu lokaci yayi tunda wasu tsirarun mutane sun rusa PDP, to dole mu tafi gidan da zamu ceci yankinmu da jiharmu baki ɗaya.

Daga karshe ya godewa dukkan masoyansa da magoya bayansa fiye da mota hamsin da s**a masa rakiya zuwa mazaɓarsa, inda ya shelanta musu komawarsa APC tare da umartar mabiyansa baki daya da su koma mazabunsu su yankin katin jam'iyyar APC don tunkarar zaɓen 2027 insha Allah.

Want your business to be the top-listed Media Company in Abuja?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Address


Nsukka Street Abuja
Abuja