Manara RADIO
LABARUN DUNIYA
GWAMNATIN NAJERIYA TA CE RAHOTON BANKIN DUNIYA KAN TASARRUFIN KUDI BA YA NUFIN A NA SAMUN TASGARO
Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa rahoton da bankin duniya ya fitar kan tasarrufin kudin shekara na Najeriya ba ya nuna karkatar da kudin gwamnati zuwa wasu lamura na daban a bayan fage.
Karamin ministan kudi Taiwo Oyedele ya bayyana haka a wata sanarwa da ke zargin wasu kafafen labaru da murde gaskiyar yadda lamarin ya ke har ma da amfani da bayanan da sun riga sun wuce.
Oyedele ya ce kudaden da a ke magana na halal ne da su ka shafi biyan basukan ayyukan da jihohi ko wasu ma’aikatu su ka gudanar da wasu hakkokin da a ka mayarwa sassan da abun ya shafa.
Karamin ministan ya ce rahoton ma na nuna a farkon shekarar bana an samu nasarar adana kudaden da a ke samu na shiga ta hanyar man fetur da hakan ke nuna gagarumar nasarar tafiyar da lamura daidai.
A nan ministan ya nanata matsayin gwamnati na tabbatar da adalci ga hanyoyin da a ke kashe kudi a shekara ta hanyar gaskiya da amana.
KAKAKIN SHUGABA TINUBU BAYO ONANUGA YA NUNA GAMSUWA CEWA A NA SAMUN GAGARUMAR NASARA KAN TSARO
Kakakin shugaba Tinubu Mr.Bayo Onanuga ya bayyana cewa ya samu gamsuwa cewa a na samun gagaruman nasarori a bangaren samar da tsaro a fadin Najeriya.
Onanuga ya ce ba k**ar yadda a ke yayata labarun da kan nuna tamkar ba a yaba kokarin jami’an tsaro soja a fagen daga, ya ce gaskiya ya samu labaru masu nuna a na cimma nasarorin yaki da miyagun iri.
Mr.Onanuga ya buga misali da labarun da ya ke samu daga kafar Zagazola cewa a na rutsawa da ‘yan ta’addan ISWAP, Boko Haram da ma ‘yan ta’addan daji.
Kakakin ya kawo wani misalin labarin da a ka yayata na sace fasinjoji 17 a wata motar safa a jihar Binuwai ciki har da amsu rubuta jarrabawar neman gurbin shiga jami’a inda 3 daga ma’abota motar su ka tsira.
Onanuga ya ce sauran mutum 14 ma an kubutar da su kuma an gano wasu miyagu ne na cikin gida na Binuwai su ka aikata mugun laifin ba ‘yan ta’addan daji ko Fulani da wasu ke ambata ba.
JAM’IYYAR APC TA FITAR DA JADAWALIN ZABUKAN FIDDA GWANI DA DUK ZA A KAMMALA A WATAN GOBE
Jam’iyyar APC mai mulki ta fitar da jadawalin sayar da fom din neman takara da zaben fidda gwani a dukkan muk**ai karkashin jam’iyyar.
Wannan dai don ya dace da kammala hada jerin sunayen ‘yan takara k**a daga majalisun jihohi, na tarayya, shugaban kasa da gwamnoni da za a mika a watan goben na Mayu.
Mafi tsadar kudin na mai son tsayawa takarar shugaban kasa ne naira miliyan 100 sai na gwamna naira miliyan 50. Masu son tsayawa takarar majalisar dattawa za su kashe miliyan 20 majalisar wakilai wakilai kuma naira miliyan 10.
Duk da haka akwai sassauci kan takarar mata, matasa da masu bukata ta musamman da za su biya kusan rabin kudin fom neman takarar.
Hukumar zabe INEC za ta fara gudanar da babban zaben 2027 daga ranar 16 ga watan Janairu mai zuwa.
TRUMP YA CE ZA A SAMU ZANTAWA MAFI DACEWA KAN TAKADDAMAR KERA MAK**AN NUKILIYA NA IRAN
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce za a samu yarjejeniya mafi dacewa ta warware takaddamar kera mak**an nukiliya na Iran.
Wannan dai sako ne k**ar yadda Trump ke yi ta hanyar kafar sadarwarsa ta yanar gizo Truth Social.
Wannan na zuwa cikin tsagaita bude wuta na mako biyu a yakin da Amurka da Isra’ila su ka aukawa Iran kimanin makonni 7 da su ka wuce.
Trump ya yi wannan bayani biyo bayan korafin da ‘yan majalisa na jam’iyyar Dimokrats su ka yi cewa Trump ya na gaggawa kan wannan yarjeniya na lamari mai muhimmanci.
Ba a tantance yadda za a cimma maslaha a dan kankanin lokaci ba amma Trump na nuna ba ya cikin matsin lamba kuma ya na da kwarin guiwar samun nasara.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the business
Telephone
Address
Utako District
Abuja