Mai Martaba
20/01/2026
SARKI SANUSI YA KOMA AJI DOMIN KARANTAR ILIMIN SHARI'A A JAMI'AR KANO
Abubakar Sadiq Galadima
A ranar Talatar nan ne Sarkin Kano, Muhammad Sanusi na II, ya fara zuwa Jami'ar Northwest, Kano, a matsayin dalibin neman ilimin zama Lauya.
Sanusi na II ya haɗu da abokan karatunsa wato sauran ɗalibai a safiyar talata, sanye da doguwar riga baƙa tare da farar hula.
Ya zauna a ajin tare da dalibai da suke aji guda wato aji biyu na tsangayar.
Matakin na zuwa ne bayan jami'ar ta yi masa tayin shiga, domin neman ƙwarewa a harkokin Shari'a.
Jam'i,’ar ta ce an yanke shawarar ne saboda gogewarsa a fannin shugabanci, tattalin arziki, da kuma hidimar jama'a.
An kafa Jami'ar Northwest a shekarar 2012, tana ɗaya daga cikin jami'o'i biyu mallakar jihar Kano.
Dawowar jami'ar ta biyo bayan kammala yin rijista kamar yadda kowani ɗalibi yake yi kafin ya shiga aji.
Sanusi II, wanda ya riga ya sami digirin digirgir (PhD), tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) ne kuma ya kasance mai fada a ji.
Kasancewarsa a harabar jami'a ta jawo farin ciki ga matasa 'yan ajinsu, waɗanda s**a bayyana wannan lokacin a matsayin alama ta darajar makarantun.
゚viralvideo
27/09/2025
Wani caption yafi dacewa da wannan hoton???
19/04/2016
Abubakar Sadeeq Galadima (Jouro Maudo)
19/04/2016
Abubakar Sadeeq Galadima Jouro Maudo
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Address
Utako