Bahaushe

Bahaushe

Share

09/10/2022

Atiku ya sauka a Jihar Uyo

Ɗan takarar shugabancin ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar PDP Atiku Abubakar ya sauka a jihar Uyo domin fara kamfen ɗin sa na zaɓen 2023.

Photos from Bahaushe's post 09/10/2022

Hotunan Gangamin Marawa Tinubu Baya ya Jawo Cunkushewar Hanyoyi a Jihar Legas.

A yanzu haka dai ana zaune a cunkushe a sassa daban-daban na jihar Legas sakamakon taron hadin kan da aka yi wa Asiwaju Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyya mai mulki ta APC.

Musiliu Akinsanya, tsohon shugaban kungiyar ma’aikatan sufurin mota ta kasa (NURTW), ya sanar da gudanar da gagarumin gangamin ne ga Tinubu sakamakon magoya Peter Obi sun yi tattaki a titunan Legas a makon jiya.

Hakan yana zuwa kusan a matsayin martani ga magoya bayan Peter Obi. Inda s**a cika titunan Legas suna kirari : “Se Jagaban”, “Tinubu don shugaban kasa” .

Wannan taro dai ya haifar da cunkushewar hanyoyi wanda hakan ya sa da ƙyar ababan hawa ke wucewa.